Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya ce Kyaututtukan Ƙanana da Matsakaitan Sana’o’i na Ƙasa na shekarar 2026 sun nuna ƙudirin Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, na mayar da ƙanana da matsakaitan sana’o’i ginshiƙin bunƙasar tattalin arzikin Nijeriya ƙarƙashin tsarin (Renewed Hope Agenda).

Ministan ya bayyana hakan ne bayan bikin karrama fitattun ‘yan kasuwa da aka gudanar a ɗakin taro na Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja a ranar Asabar.

Ya ce karramawar da aka yi wa fitattun masu sana’o’i na nuna ƙudirin Gwamnatin Tarayya na samar da yanayi mai kyau da zai baiwa kasuwanci damar bunƙasa, samar da ayyukan yi da kuma ƙarfafa ci gaban tattalin arziki mai ɗorewa.

Ministan yace rabon tallafin Naira biliyan ɗaya ga ƙananan ƴan kasuwa zai ƙarfafa ƙananan sana’o’i tare da bunƙasa tattalin arziƙi.

Ya buƙaci waɗanda suka amfana da tallafin su yi amfani da shi wajen faɗaɗa kasuwancinsu, da taimaka wa sauran masu tasowa da kuma samar da ayyukan yi.

Mohammed ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da haɗa kai da jihohi da kamfanoni masu zaman kansu, domin bunƙasa harkokin kasuwanci da tattalin arzikin ƙasa.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *