Tawagar ƙwallon ƙafa ta Senegal ta fice daga Gasar Kofin Duniya bayan ta sha kashi a hannun Belgium da ci 3-2 a wasan zagaye na 32.

Senegal ce ta fara cin ƙwallaye biyu ba tare da an zura mata ko ɗaya ba, kuma ta ci gaba da jan ragamar wasan har zuwa mintuna na ƙarshe.

Sai dai Belgium ta yi nasarar farke ƙwallayen biyu kafin cikar lokacin wasa, lamarin da ya sa aka tafi ƙarin lokaci.

A ƙarin lokacin ne Belgium ta samu bugun fenariti, inda ta zura ƙwallo ta Uku, ta tabbatar da nasarar ta tare da samun tikitin zuwa zagayen ‘yan 16, yayin da Senegal ta yi bankwana da gasar.

A wani wasan kuma, tawagar Amurka ta samu nasarar doke Bosnia, lamarin da ya ba ta damar tsallakawa zuwa zagaye na gaba na gasar.

Kawo yanzu kasashen Amurka, Norway, Ingila, Brazil da Belgium sun samu tsallakawa zuwa zagaye na gaba.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *