Babban Jami’in Gudanarwa na Hukumar Kula da Harkokin Mai ta NMDPRA, Mallam Rabiu Abdullahi Umar, ya ce manufar hukumar ba bin doka kaɗai ba ne, har ma da samar da yanayi mai kyau da zai ƙarfafa amincewar masu zuba jari.

Ya bayyana haka a wajen Taron Manyan Lauyoyi da Mashawartan Shari’a na shekarar 2026 da aka gudanar a Abuja.

Ya ce taron ya zama wata muhimmiyar hanya ta ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumar da kamfanonin da ke da lasisin gudanar da harkokin man fetur.

Shi kuma Mashawarcin Shari’a na hukumar, Dr. Joseph Tolorunse, ya ce bin doka shi ne ginshiƙin tsarin sa ido, amma babban buri shi ne samar da yanayin da masu zuba jari za su samu tabbacin gudanar da kasuwanci cikin adalci, da gaskiya da daidaito.

Ya ƙara da cewa hakan ne zai taimaka wajen gina masana’antar man fetur mai ƙarfi, da gasa da kuma jan hankalin masu zuba jari daga sassa daban-daban na duniya.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *