Najeriya ta shafe shekara 20 ba tare da gudanar da sabon ƙidayar jama’a da gidaje ba tun bayan wanda aka yi a shekarar 2006.

Lamarin ya sa ƙasar ke ci gaba da tsara manufofi da kasafin kuɗi bisa hasashen yawan jama’a maimakon sahihan alkaluma.

Yayin da ake tunkarar babban zaɓen shekarar 2027, har yanzu ba a bayyana ranar gudanar da sabuwar ƙidayar jama’a ba.

Masana na cewa rashin sabbin bayanan ƙidaya na iya shafar tsare-tsaren gwamnati da zuba jari da ayyukan ci gaba.

Haka kuma, hukumomi da abokan hulɗar cigaba na ci gaba da dogaro da kiyasin yawan jama’a wajen yanke muhimman shawarwari.

Ana ganin gudanar da sabuwar ƙidayar jama’a zai samar da ingantattun bayanai da za su taimaka wajen tsara manufofin ci gaban ƙasa da raba albarkatu cikin adalci.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *