Majalisar Tarayya ta mika Kudirin Gyaran Kundin Tsarin Mulki da ke neman kafa Rundunonin ‘Yan Sandan Jihohi zuwa Majalisun Dokoki na Jihohi 36 domin dubawa da amincewa.

Akawun Majalisar Tarayya, Kamoru Ogunlana, ya bayyana cewa an mika kudirin zuwa Majalisun Jihohin ne a ranar Laraba, 16 ga Satumba, 2026, tare da tsammanin cewa za su gudanar da kyakkyawan bincike kan kudirin cikin sauri har zuwa tsawon wata guda.

Koda yake Kundin Tsarin Mulki bai kayyade takamaiman lokacin da Majalisun Jihohin za su mayar da martani ba, Majalisar Tarayya tana tsammanin za su sanar da matsayarsu tsawon kwanaki 30 bayan karbar kudirin.

Sai dai kuma, Akawun ya fito fili ya bayyana cewa tsawon kwanaki 30 din gudanarwa ne kawai na tafiyar da aiki, ba wai ka’ida ce ta tsarin mulki ba.

​Majalisar Tarayya ta ce tana girmama alhakinsu na tsarin mulki da kuma ‘yancin Majalisun Dokokin Jihohi wajen yin nazari kan gyare-gyaren da ake shirin yi.

​A karkashin tanadin tsarin mulki, dole ne kudirin da ke neman sauya Kundin Tsarin Mulki ya samu amincewar a kalla kashi biyu cikin uku (2/3) na Majalisun Dokoki na Jihohi 36 kafin a kammala tsarin.

​Duk da haka, Majalisun biyu na kasar sun kaddamar da Kudirin ‘Yan Sandan Jiha makonni kadan da suka gabata, a matsayin wani muhimmin mataki na tunkarar kalubalen tsaro a kasar.

​Majalisar Tarayya ta ce za ta ci gaba da daukar matakai na gaba da zarar ta karbi matsaya daga Majalisun Jihohi, yayin da take jaddada jajircewarta ga tsari na gaskiya, hadin gwiwa tsakanin ma’aikatu, da kuma bin Kundin Tsarin Mulki sau da kafa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *