Karfafa sanya ido kan iyakoki da filayen sauka da tashin jirage

Cibiyar Kula da Cututtuka da Kare Aukuwarsu ta Nijeriya (NCDC) ta ce ta ƙara ƙarfafa shirye-shiryenta na dakile yiwuwar ɓarkewar cutar Ebola a ƙasar, bayan ƙaddamar da Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Yaƙi da Cutar Ebola.

Darakta Janar na Hukumar, Dr. Jide Idris, ya jagoranci tarurrukan wasu ƙananan kwamitoci da ke da alhakin sa ido kan cututtuka, gwaje-gwaje, kula da marasa lafiya, da kuma samar da kayan aiki domin tunkarar barazanar cutar.

NCDC ta ce tarurrukan sun mayar da hankali ne kan ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomi, inganta tsarin gano masu ɗauke da cutar da wuri, shirya dakunan gwaje-gwaje, kula da masu kamuwa da cutar, tattara kayan aiki da kuma tura ƙwararrun ma’aikata domin tabbatar da cikakken shiri.

Hukumar ta bayyana cewa matakan sun zama wajibi ne sakamakon ci gaba da ɓarkewar cutar Ebola a ƙasashen Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo da Uganda, domin hana yiwuwar bazuwar ta zuwa Nijeriya.

Taron ya samu halartar wakilai daga Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya, NCDC, Hukumar Kula da Lafiya a kan iyakoki, Hukumar Filayen Jiragen Sama ta Nijeriya (FAAN), Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) da sauran hukumomi da ƙungiyoyin da ke da ruwa da tsaki a fannin lafiya.

 

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *