Wata yarinya mai shekaru 19 na daga cikin mutane uku da suka rasu sakamakon shaƙewar numfashi yayin bikin murnar cin gasar Kofin Duniya a birnin Mexico a ranar Talata.

Haka kuma wata mata mai shekaru 48 da wani namiji mai shekaru 44 sun mutu bayan da birnin ya cika makil, bayan da ƙasar ta doke Ecuador da ci 2–0, kamar yadda hukumar lafiya ta babban birnin ta bayyana a ranar Laraba.

Gwamnan birnin, Clara Brugada, ta mika ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka rasu tare da alƙawarin ba su tallafi a kwanaki masu zuwa.

Hukumomin lafiya sun ce ma’aikatan agajin gaggawa sun kula da mutane uku da suka suma a wurare daban-daban a kan titin Paseo de la Reforma, kafin a kai su asibiti.

Nasarar ranar Talata ta tura Mexico zuwa zagaye na 16 a Kofin Duniya, inda za su iya haduwa da Ingila idan ƙungiyar Thomas Tuchel ta doke Jamhuriyar Kwango a ranar Laraba.

Fiye da mutane miliyan ɗaya ne suka fito kan tituna, musamman a kusa da dandalin Angel of Independence, da ke tsakiyar birnin.

Wannan ce nasarar farko da Mexico ta samu a zagayen fidda da gwani na Kofin Duniya tun shekarar 1986, kamar yadda gwamnatin birnin ta bayyana.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *