Hukumar Raba Shaidar Zama Ɗan Ƙasa (NIMC) ta ce ta fara shirin zagayawa dukkan mazaɓu 8,809 na ƙasar domin yi wa ‘yan Najeriya rajistar Lambar Shaidar Zama Ɗan Ƙasa (NIN).
Darakta Janar ta hukumar, Dakta Abisoye Coker-Odusote, ta ce an fara shirin ne bisa umarnin Shugaba Bola Tinubu don tabbatar da cewa babu wani ɗan Najeriya da za a bari a baya wajen cin gajiyar shirye-shiryen gwamnati.
- Majalisar Wakilai ta yi fatali da buƙatar gayyato Tinubu
- Gwamnatin Tarayya na ƙara ƙaimi wajen yi wa ‘yan Najeriya rajistar NIN –Minista
Ta ce shirin zai shafi mata da yara da masu buƙata ta musamman da mazauna karkara da’yan gudun hijira da baƙi masu izinin zama da kuma ‘yan Najeriya mazauna ƙasashen waje.
Ta kuma ce sabuwar dokar NIMC ta 2026 za ta ƙarfafa kariyar bayanan jama’a da tsaro ta intanet da kuma yaƙi da damfara ta hanyar amfani da bayanan sirri.