Ɗaya daga cikin manyan jagororin adawa a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo (DR Congo), Delly Sesanga, ya ce jami’an gwamnati sun hana shi barin ƙasar tare da ƙwace fasfo ɗinsa, lamarin da ya bayyana a matsayin wani yunkuri na tsoratarwa da kuma takura masa.
Sesanga, shugaban jam’iyyar Envol, tsohon minista kuma tsohon ɗan majalisa, na daga cikin jagororin sabuwar ƙungiyar adawa da ke ƙin shirin gwamnatin Shugaba Félix Tshisekedi na sauya kundin tsarin mulki.
A farkon watan nan ne majalisar dokokin ƙasar ta amince da kudirin dokar gudanar da ƙuri’ar raba gardama kan gyaran kundin tsarin mulki, masu adawa na zargin cewa wannan mataki zai bai wa Shugaba damar sake tsayawa takara karo na uku duk da cewa wa’adinsa na biyu zai ƙare a watan Disamba a shekara ta 2028, a ranar 12 ga Yuni, jami’an tsaro sun tarwatsa zanga-zangar adawa da aka gudanar a birnin Kinshasa domin nuna adawa da abin da masu zanga-zangar suka kira “yunƙurin juyin mulki ta hanyar kundin tsarin mulki.
-
Trump: Amurka ta kawo ƙarshen kisan kirista a Najeriya.
-
FCCPC ga ’yan kasuwa: Ku sauƙaƙe farashin man fetur ko ku fuskanci takunkumi