Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun farfado da kokarin su, yayin da suka nuna jajircewa wajen doke Zambia da ci 1-0 don kare kambun su ta Gasar cin Kofin Mata na Nahiyar Afirka (WAFCON) a wasan rukuni na C mai cike da tashin hankali da kuma fargaba.
Super Falcons ta buga fiye da rabin wasan da ’yan wasa 10, a filin wasa na Al Madina da ke Rabat bayan an bai wa ’yar wasan baya, Blessing Demehin, jan kati a minti na 40 saboda ta fadar da kyaftin din Zambia, Barbra Banda, a kasa yayin da Copper Queens ke neman farke kwallon da aka zura musu.

A halin yanzu, Super Falcons ta samu maki uku mai muhimmanci sakamakon doke ta ci 3-2 a wasan ta na farko da ta buga da Malawi.
- Zaben NFF: Za a fara sayar da fom ranar Asabar 1 ga Agusta
- WAFCON 2026: Yadda Algeria da Kenya suka sha kaye a hannun Moroko da Senegal
- WAFU B U20: Flying Eagles sun lallasa Sparrow Hawks da ci 3-0
Kwallon da Asisat Oshoala ta ci da wuri a minti na takwas ita ce ta tabbatar da nasarar yayin da masu rike da kambun, wato Najeriya, ta samu maki uku na farko a gasar bayan shan kaye a wasan bude wa da Malawi.

Wannan sakamako ya sa rukuni na C ya kasance cike da tashin hankali da kuma fargaba kafin wasan rukuni na karshe.
A halin yanzu, Malawi na jagorantar teburin da maki 6 bayan nasara biyu a jere, yayin da Najeriya da Zambia ke da maki 3 kowacce. Egypt kuma ba ta da maki ko daya.
Najeriya za ta buga da Egypt a wasan karshe na rukuni a ranar Laraba, yayin da Malawi da Zambia za su buga wasan karambarta na kasashe ‘yan Kudancin Afirka domin neman gurbin shiga wasan Kwata-fainal.