Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Sakkwato ta ce ta samu nasarar kuɓutar da dukkan mutanen da aka sace a hare-hare biyu da ‘yan bindiga suka kai a ƙananan hukumomin Rabah da Binji.

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, Hayatu Hassan Shaffa, ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar hedkwatar rundunar a Sakkwato

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, Hayatu Hassan Shaffa, ya ce jami’an rundunar tare da haɗin gwiwar sojoji sun yi artabu da ‘yan bindigar, lamarin da ya tilasta musu tserewa zuwa cikin daji tare da ceto waɗanda aka yi garkuwa da su ba tare da sun ji rauni ba.

Ya kuma bayyana cewa a wani samame da aka kai a Bodinga da kuma Daraye da ke Wamakko, jami’an tsaro sun kashe wasu ‘yan bindiga huɗu tare da ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 biyu da alburusai masu rai.

A cewarsa, rundunar za ta ci gaba da matsa wa masu aikata laifuffuka domin tabbatar da zaman lafiya a jihar.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *