A halin yanzu, rundunar ‘Yan Sandan Jihar Sakkwato ta ce ta kama mutane da dama da ake zargi da hannu a ayyukan ta’addanci, ciki har da masu garkuwa da mutane da masu bai wa ‘yan bindiga bayanan sirri da masu kai musu man fetur da kuma masu safarar miyagun ƙwayoyi.

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, Hayatu Hassan Shaffa, ya ce daga cikin waɗanda aka kama akwai mutane uku da suka amsa laifin shiga ƙungiyar masu garkuwa da mutane da ke addabar wasu ƙananan hukumomi a jihar.

Ya ce jami’an rundunar sun kuma kama wani da ake zargi da kai wa ƙungiyar Lakurawa man fetur da sauran kayayyaki, inda aka ƙwato galan-galan na fetur da tabar wiwi da ƙwayoyin Tramadol.

Shaffa ya ƙara da cewa rundunar ta kuma kama wasu da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi da kuma masu satar babur.

Kwamishinan ya yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai domin yaƙi da miyagun laifuffuka a fadin jihar.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *