Ministan Kudi kuma Ministan da ke kula da tattalin arzikin ƙasa, Taiwo Oyedele, ya ce babban ƙalubalen da Nijeriya ke fuskanta a bangaren tara kudaden shiga shi ne ƙarancin masu biyan haraji, ba wai yawan kuɗin harajin da ake karɓa ba.
Oyedele ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a Abuja yayin da yake karɓar shugabannin Cibiyar Kwararrun Masana Harkokin Haraji ta Nijeriya bayan kammala bikin ranar wayar da kan jama’a kan haraji na farko da cibiyar ta shirya.
Ya ce ɗaya daga cikin manyan matsalolin da ke hana inganta tsarin biyan haraji a ƙasar shi ne yadda mutane da dama ke kallon cewa duk lokacin da gwamnati ta yi magana kan haraji, tana neman ƙarin kuɗi ne kawai daga hannun jama’a.
- Ƙudirin kafa ’yan sandan jihohi na ƙara samun goyon baya a Nijeriya
- ’Yan sanda sun ceto mutum 9 daga hannun ‘yan bindiga a Kaduna, jami’ai biyu sun rasa rayukansu
- CBN ta umarci bankuna su daskarar da asusun mutanen da ake zargi da ɗaukar nauyin ta’addanci
A cewar sa, Najeriya har yanzu ba ta samun isassun kuɗaɗen shiga daga haraji, yana mai jaddada cewa abin da gwamnati ke nema shi ne tabbatar da cewa duk wanda ya kamata ya biya haraji ya yi hakan, domin samar da adalci a tsarin tara kuɗaɗen shiga.
Ministan ya ƙara da cewa idan aka gyara tsarin haraji yadda ya kamata, hakan zai taimaka matuƙa wajen bunƙasa ci gaban ƙasa.
Ya kuma buƙaci cibiyar ta samar da lambobin yabo na shekara-shekara domin karrama mutanen da suka fi bin doka wajen biyan haraji, a matsayin wata hanya ta ƙarfafa wa mutane gwiwar riƙa biyan haraji da kansu.
Wannan na zuwa ne shekara guda bayan Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya rattaba hannu kan dokokin gyaran tsarin haraji na Nijeriya a ranar 26 ga watan Yunin shekarar 2025, wani mataki da gwamnati ke ganin zai taimaka wajen inganta tattalin arzikin ƙasa.
