Ƙungiyoyin masu aikin ceto na ci gaba da neman waɗanda suka tsira da suka maƙale a ƙarƙashin baraguzan gine-ginen da suka rushe, bayan da manyan girgizar ƙasa biyu suka afku a jere a Venezuela.
Ministan Lafiya na ƙasar ya bayyana cewa aƙalla mutane 235 sun mutu, yayin da wasu 4,300 suka jikkata.
Mafi yawan waɗanda abin ya shafa sun fito ne daga yankin gaɓar teku na arewacin ƙasar, La Guaira
- Kenya ta tsaurara tsaro yayin da aka cika shekaru biyu da zanga-zangar matasan Gen Z
- Girgizar ƙasa mai ƙarfi ta kashe mutum 32 tare da jikkata ɗaruruwa a Venezuela
- Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026: Afirka ta Kudu, Morocco sun kai zagaye na 32
Ƙasashe da ƙungiyoyin duniya sun yi ta miƙa tayin tallafi da agajin jin ƙai bayan girgizar ƙasa mai ƙarfi ta maki 7.2 da 7.5 ta afku
Shugabar riƙon ƙwarya, Delcy Rodríguez, ta ayyana dokar taɓaci a faɗin ƙasar, tana mai cewa Filin Jirgin Sama na Simon Bolivar International da ke babban birnin ƙasar, Caracas, an rufe shi saboda irin barnar da girgizar ƙasar ta yi.