Ƙungiyoyin masu aikin ceto na ci gaba da neman waɗanda suka tsira da suka maƙale a ƙarƙashin baraguzan gine-ginen da suka rushe, bayan da manyan girgizar ƙasa biyu suka afku a jere a Venezuela.

Ministan Lafiya na ƙasar ya bayyana cewa aƙalla mutane 235 sun mutu, yayin da wasu 4,300 suka jikkata.

Mafi yawan waɗanda abin ya shafa sun fito ne daga yankin gaɓar teku na arewacin ƙasar, La Guaira

Ƙasashe da ƙungiyoyin duniya sun yi ta miƙa tayin tallafi da agajin jin ƙai bayan girgizar ƙasa mai ƙarfi ta maki 7.2 da 7.5 ta afku

Shugabar riƙon ƙwarya, Delcy Rodríguez, ta ayyana dokar taɓaci a faɗin ƙasar, tana mai cewa Filin Jirgin Sama na Simon Bolivar International da ke babban birnin ƙasar, Caracas, an rufe shi saboda irin barnar da girgizar ƙasar ta yi.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *