Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Abdulrazak Sa’ad Namdas a matsayin sabon Darakta Janar na Hukumar Raya Al’ummomin Kan Iyaka (Border Communities Development Agency – BCDA).
Gidan Rediyon VON ya ruwaito cewa Namdas ya maye gurbin Dakta Dakorinama Alabo George, wanda ya yi murabus domin tsayawa takarar mukamin siyasa a jihar sa.
Haka kuma, Shugaban ƙasa ya naɗa Hon. Patrick Obahiagbon a matsayin Darakta Zartarwa mai kula da Tsare-tsare da Kasuwanci a Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Neja Delta (Niger Delta Power Holding Company – NDPHC).
- Ƙungiyar Musulmi ta bukaci a sauke farashin mai zuwa ƙasa da N700 a kowace lita
- Ku zo mu yi aikin gina mafita mai ɗorewa ga halin da yaran Arewa ke ciki—IG Wala
- NAFDAC ta gargadi ’yan Najeriya kan wasu abubuwan sha masu kuzari da aka haramta a Ghana
Obahiagbon ya maye gurbin Injiniya Omoregie Ogbeide-Ihama, wanda shi ma ya yi murabus domin tsunduma harkokin siyasa.
Tinubu ya kuma sake naɗa Mr. Chukwuma Umeoji a matsayin Darakta Zartarwa mai kula da Harkokin Gudanarwa (Corporate Services) na hukumar NDPHC.
Dukkan waɗannan naɗenaɗen dai sun fara aiki nan take.