Hukumar Yaƙi da Masu Yi wa Tattalin Arzikin Ƙasa Ta’annati (EFCC) ta ce ta kwato sama da Naira biliyan 38.66 da kadarori a wani bincike da take gudanarwa kan zargin karkatar da kuɗaɗen da aka ware domin gyaran matatun man fetur na gwamnati.

Hukumar ta ce akwai yiwuwar wasu tsofaffi da masu riƙe da muƙamai a Kamfanin Man Fetur na Nijeriya (NNPCL) da wasu ‘yan kwangila za su fuskanci shari’a.

Binciken ya shafi kuɗaɗen da suka kai kusan dala biliyan 2.79 da aka kashe tsakanin shekarun 2021 da 2023 domin gyaran matatun mai na Fatakwal, da Warri da Kaduna.

EFCC ta ce ta kwato Naira biliyan 9.4 da dala miliyan 21.2, baya ga wasu kadarorin ƙasa da ake zargin suna da alaƙa da mutanen da ake bincike.

Rahotanni sun nuna cewa duk da biliyoyin dalolin da aka kashe wajen gyaran matatun mai, ba a samu gagarumin ci gaba a ayyukansu ba. Hakan ya ƙara ƙarfafa zargin cewa an karkatar ko kuma an wawure wani ɓangare mai yawa na kuɗaɗen da aka ware domin ayyukan.

EFCC ta ce binciken ya kai ga tambayar sama da manyan jami’ai 30 na NNPCL da kuma jami’ai fiye da 50 na kamfanonin da suka karɓi kwangilolin gyaran matatun mai.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *