Ministan Albarkatun Man Fetur, Heineken Lokpobiri, ya ce samun tabbataccen tsarin dokoki, da daidaito da kuma gaskiya a fannin man fetur na da matuƙar muhimmanci wajen ƙarfafa gwiwar masu zuba jari a Nijeriya.

Ya bayyana hakan ne a wajen buɗe Taron Manyan Lauyoyi da Mashawartan Shari’a na shekarar 2026 da aka gudanar a Abuja, inda ya yaba wa Hukumar NMDPRA bisa samar da dandalin tattaunawa tsakanin hukumomin da ke sa ido da kamfanonin da ke gudanar da harkokin man fetur.

Lokpobiri ya ce aiwatar da Dokar Masana’antar Man Fetur ta shekarar 2021 da kuma sassauta dokokin kasuwar man fetur sun taimaka wajen ƙara ƙarfin tace mai a cikin ƙasa, da inganta wadataccen man fetur da kuma samar da sabbin hanyoyin zuba jari.

Ya kuma buƙaci mashawartan shari’a su ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen inganta shugabanci, da ƙarfafa zuba jari cikin gaskiya da kuma bunƙasa masana’antar man fetur a Nijeriya.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *