Wasu fitattun ‘yan wasan ƙwallon ƙafa da suka daɗe suna wakiltar ƙasashensu sun kammala wasansu na ƙarshe a Gasar Kofin Duniya ta 2026, bayan ƙasashensu sun fice daga gasar.

Cikin ‘yan wasan akwai Cristiano Ronaldo na Portugal da Neymar na Brazil da Riyad Mahrez na Aljeriya da Guillermo Ochoa na Mexico da Manuel Neuer na Jamus.

Ronaldo ya bayyana tun kafin wasan Portugal da Spain cewa wannan ne Kofin Duniya na ƙarshe da zai buga.

Portugal ta fice ne bayan ta sha kashi da ci 1-0 a hannun Spain a zagayen ‘yan 16.

Shi ma Neymar ya tabbatar bayan an fitar da Brazil daga gasar cewa ya kawo ƙarshen taka leda a matakin ƙasa da ƙasa, yayin da Mahrez ya sanar da yin ritaya daga tawagar Aljeriya bayan sun sha kashi a hannun Switzerland.

Haka kuma Guillermo Ochoa ya nuna alamun yin ritaya daga ƙungiyar ƙasarsa bayan ficewar Mexico, yayin da Manuel Neuer ya ce bai yi nadamar komawarsa tawagar Jamus ba duk da ficewarsu daga gasar.

Sai dai wasu fitattun ‘yan wasa irin su Lionel Messi na Argentina da Luka Modric na Croatia ba su sanar da yin ritaya ba, duk da cewa ana hasashen Gasar Kofin Duniya ta 2026 na iya kasancewa ta ƙarshe a gare su.

 

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *