Rundunar haɗin gwiwa ta Operation Hadin Kai (OPHK) ta sanar da samun sabbin nasarori a yaƙin da take yi da ƙungiyoyin ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas, inda ta ceto ƙarin mutane da aka sace tare da dakile wani hari da mayaƙan ISWAP suka kai sansanin soji da ke Logomani a jihar Borno.

A cikin wata sanarwa da Muƙaddashin Jami’in Yaɗa Labarai na rundunar, Kyaftin Mohammed Goni, ya fitar, ya ce a ranar 7 ga Yuli, 2026, sojojin Bataliya ta 115 sun ceto ƙarin mutane biyu daga maboyar ‘yan ta’adda a ƙaramar hukumar Askira/Uba.

Sanarwar ta ce yayin aikin, sojojin sun kuma ƙwace kuɗi har Naira miliyan 1.2 da ake zargin haramtun kuɗaɗen ne, tare da kayan abinci da sauran kayayyakin da ake amfani da su wajen tallafa wa ayyukan ta’addanci.

Ta ƙara da cewa an kai waɗanda aka ceto wurin da ya dace domin ba su kulawar lafiya da kuma tallafin ƙwararrun likita.

 

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *