Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA) ta ce za ta yi aiki kafaɗa da kafaɗa da Hukumar NIMC domin wayar da kan al’umma kan muhimmancin yin rajistar Lambar Shaidar Zama Ɗan Ƙasa (NIN).

Darakta Janar na hukumar, Mallam Lanre Issa-Onilu, ya bayyana haka yayin ganawar da jami’an NIMC suka yi da Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai a Abuja.

Ya ce kasancewar NOA tana da ofisoshi a dukkan ƙananan hukumomi 774 na ƙasar zai taimaka wajen isar da saƙon gwamnati ga al’ummomin karkara da waɗanda ba su da sauƙin samun bayanai.

Ya ƙara da cewa haɗin gwiwar zai tabbatar da cewa kowane ɗan Najeriya ya fahimci amfanin rajistar NIN kuma ya samu damar cin gajiyar shirye-shiryen gwamnati.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *