Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa EFCC ta samu nasara a shari’ar ƙwace kadarorin da ake alaƙanta wa da tsohon Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami (SAN), bayan kusan watanni shida da ta fara shari’a.

Mai Shari’a Joyce Abdulmalik ta Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci a ƙwace kadarori 48 tare da mayar da su hannun Gwamnatin Tarayya, bayan amincewa da buƙatar EFCC.

A cikin wata sanarwa, EFCC ta ce tun a ranar 6 ga Janairun 2026 ne ta fara samun umarnin wucin gadi na ƙwace kadarorin daga kotu, sannan ta wallafa sanarwa tana gayyatar duk masu ruwa da tsaki su bayyana dalilan da ya sa bai kamata a ƙwace kadarorin ba.

Sai dai bayan sauraron ƙorafe-ƙorafen Malami da wasu mutum 14 da suka haɗa da ‘yan uwansa da abokan hulɗarsa, kotun ta tabbatar da ƙwace kadarorin baki ɗaya.

Daga cikin kadarorin da aka ƙwace akwai Jami’ar Rayhaan da ke Jihar Kebbi da Rayhaan Radio da otal-otal da gidaje da masana’antu da tashar mai da filaye a jihohin Kebbi da Kano da Babban Birnin Tarayya Abuja.

EFCC ta bayyana hukuncin a matsayin wani gagarumin ci gaba a ƙoƙarinta na ƙwato kadarorin da ake zargin an mallake su ta hanyar haramtacciyar hanya.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *