Rundunar ’Yan Sandan Jihar Sokoto ta sanar da sake fara aikin duba ababen hawa daga ranar Alhamis, 13 ga Agusta, 2026, domin tabbatar da bin dokokin hanya da ƙara inganta tsaro a kan titunan jihar.

Rundunar ta ce za ta fi mayar da hankali kan motocin da ba su da izinin amfani da gilashin mota mai duhu da masu tuki ta hanyar da ta sabawa hanya wato “One-Way”, da kuma motocin da ba su da cikakkiyar rajista.

Haka kuma, rundunar ta ce za a hukunta masu amfani da lambobin mota na bogi ko na jabu da motocin da lambobinsu suka kasance a rufe da lanƙwasa ko kuma ba a iya karantawa yadda ya kamata.

Sauran laifukan da rundunar ta ce za ta tsaurara matakan yaki da su sun haɗa da tukin ganganci da ɗaukar kaya ko fasinjoji fiye da kima da rashin bin alamomin hanya da kuma tukin mota ba tare da ingantaccin lasisin tuƙi ba.

Kwamishinan ’Yan Sandan Sokoto, CP Hayatu Hassan Shaffa, ya ce za a gudanar da aikin cikin nuna ƙwarewa da mutunta haƙƙin jama’a. Ya kuma gargadi jami’an da aka tura aikin da kada su ci zarafi da tsoratarwa ko karɓar kuɗi ba bisa ƙa’ida ba.

Rundunar ta buƙaci masu ababen hawa su tabbatar motocinsu suna da cikakkun takardu, su cire duk wani abin da ke rufe lambar mota, su mallaki ingantaccen izinin gilashin mota mai duhu idan ya dace, sannan su guji tuƙin aron hannu.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *