Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce Gwamnatin sa na da burin ninka gudunmawar da take bayarwa ɓangaren kiwon dabbobi, daga sama da dala biliyan 32 da ake samarwa a yanzu.
Shugaban ya bayyana hakan ne a Abuja yayin buɗe taron ƙasa da ƙasa karo na 9 kan kiwon dabbobi a Afirka, wanda Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ya wakilta.
Tinubu ya ce ɓangaren kiwo na taka muhimmiyar rawa wajen samar da abinci da ayyukan yi da damar bunƙasar tattalin arziki, inda ya bayyana cewa Najeriya na da sama da Shanu miliyan 58 da Tumaki miliyan 64 da Awaki miliyan 124 da kuma Kaji sama da miliyan 660.
- Ƙungiyar Musulmi ta Duniya ta shirya taron tsaro na ƙasa da ƙasa a Abuja
- Juyin Mulki: na yi abin da na yi ne saboda kishin ƙasa — Kanal Ma’aji
Ya ce gwamnati na aiwatar da shirye-shirye domin sauya harkar kiwo daga tsarin gargajiya zuwa kiwo na zamani mai amfani da fasaha, domin jerawa da kasashen duniya.
Shugaban ya ce gwamnatin sa, na shirin ƙara yawan jari a bangaren samar Madarar Nono da sarrafa nama, fatu da abincin dabbobi.
Tinubu ya ce gwamnati, na son rage dogaro da kasashen waje, domin shigo da madara, inda shirin ƙara adadin madarar da ake samar wa a cikin gida ke cigaba da fadada.
Ya ƙara da cewa harkar kiwo na da damar samar da miliyoyin ayyukan yi, musamman ga matasa da mata, ta hanyar inganta damar samun kuɗaɗen jari, fasahar zamani da haɗin gwiwa da kamfanoni masu zaman kansu.
Shugaban ya kuma jaddada buƙatar haɗin kan ƙasashen Afirka wajen magance matsalolin cututtukan dabbobi da sauyin yanayi da ƙarancin abinci da matsalolin cinikayyar dabbobi da ke ƙetare iyakokin ƙasashe.
Ya ce Najeriya a shirye take ta yi aiki da sauran ƙasashen Afirka da abokan hulɗa, domin mayar da nahiyar Afirka cibiyar samar dabbobi da duniya ke bukata.