Wasan da Arsenal ke shirin bugawa da West Ham a Filin Wasa na Landan Stadium yana da matukar muhimmanci.
A yanzu haka dai Gunners din suna da maki biyu ne kacal tsakaninsu da Manchester City a saman tebur tare da sauran wasanni uku.
Kuma kungiyar ta Mikel Arteta ta san cewa nasara a kan West Ham za ta sanya su a kan hanyar lashe kambun Gasar Firimiya na farko a cikin shekaru ashirin.
- Gasar Firimiya: Arsenal za ta kai labari kuwa?
- AFCON 2025: Wanne tasiri hukuncin Kotun Wasanni ta duniya zai yi?
- Kotu ta dage shari’ar takarar Goodluck Jonathan a zaben 2027
Nasarar da City ta yi a kan Brentford ranar Asabar ce ta rage tazarar da ke tsakanin kungiyoyin biyu zuwa maki biyu kacal.
Amma nasarar Arsenal a wannan wasan za ta dawo da tazara ta maki biyar.
Hakan zai tilasta wa City yin nasara a duk sauran wasanninta da suka rage — da Crystal Palace da Bournemouth da kuma Aston Villa — idan har tana son lamo Arsenal a wannan fafutukar.
Manazarta wasanni sun yi ha sashen cewa idan Arsenal ta yi nasara a wannan fafatawa, yiwuwar ta lashe kambun za ta haura kashi 80 cikin 100.
Idan kuma suka yi canjaras, to yiwuwar za ta ragu zuwa kusan kashi 60 cikin 100, lamarin da zai bai wa City damar kwace kambun, sannan idan suka sha kashi, yiwuwar za ta yi ƙasa da kashi 40 cikin 100.
Wasannin Arsenal sun fi sauƙi, domin suna da abokan hamayya biyu da ke cikin haɗarin fadawa relegation.
Wasannin Manchester City za su fi zafi – amma fa ’yan wasan Pep Guardiola sun saba da irin wannan matsin lamba a fafutukar lashe Gasar Firimiya.
Wannan wasan ba don maki uku kawai Arsenal za ta buga shi ba.
Zai kuma yi nunu da ƙarfi, da tunani, da ikon kungiyar na yin yadda take so a Gasar.
Idan Arsenal ta yi nasara, za ta karɓi cikakken iko a fafutukar lashe kambun. Idan ta yi kuskure, damar Manchester City ta kwace kambun za ta karu matuka.
