Hull City ta fara kakar gasar Premier League ta 2026/27 da gagarumar nasara, bayan ta doke Manchester United da ci 2–0 a wasan da suka fafata.

Hull City ta nuna ƙarfi tun farkon wasan, inda ta yi amfani da ƙwallayen da aka samo daga kai hare-hare ta gefen fili da kuma bugun tazara, abin da ya jefa Manchester United cikin matsala.

Semi Ajayi da Nobel Mendy ne suka zura ƙwallayen biyu da suka bai wa Hull City damar tafiya hutun rabin lokaci tana kan gaba da ci 2–0.

Bayan dawowa hutun rabin lokaci, Manchester United ta yi ƙoƙarin farfaɗowa, inda ‘yan wasanta suka ƙara matsa lamba tare da ƙoƙarin samar da damammaki a gaban ragar Hull City.

Sai dai yan wasan Hull sun ci gaba da kasancewa cikin tsari, inda suka hana United samun damar da za ta iya sauya sakamakon wasan.

Kocin Manchester United, Michael Carrick, ya yi wasu sauye-sauye ciki har da shigar da Kobbie Mainoo da Benjamin Šeško, amma sauye-sauyen ba su haifar da canjin da ake bukata ba.

Hull City kuwa ta ci gaba da nuna ƙwazo wajen kare ragarta da kuma dakile hare-haren United har zuwa ƙarshen wasa.

Daga bisani aka tashi wasan Hull City 2, Manchester United 0.

Wannan nasara ta kasance ta musamman ga Hull City, domin ita ce nasararta ta farko a kan Manchester United a gasar lig cikin shekaru 52.

Magoya bayan Hull City sun yi shagali bayan wasan, inda suka nuna farin ciki da yadda ƙungiyarsu ta fara kakar bana da babbar nasara.

A gefe guda, sakamakon ya kasance mummunan farawa ga Manchester United, wadda za ta nemi gyara kura-kurenta a wasannin da ke tafe.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *