Kashim Shatima da sauran muƙarraban Gwamnati wajen kaddae da ruwansha a Abuja

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ayyana kawo ƙarshen matsalar ruwa a wasu garuruwan da ke kewaye da Babban Birnin Tarayya Abuja (FCT).

Shugaban ya bayyan hakane yayin ƙaddamar da tsarin samar da ruwan sha ga al’ummomin Karu, Orozo, Jikwoyi, Kurudu da sauran yankunan da ke maƙwabtaka da su

Shugaban, wanda Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya wakilta, ya ce wannan aiki na nuna ƙudirin Ajandar Sabon Fata (Renewed Hope Agenda) wajen samar da muhimman ayyuka da hidimomi, kare martabar jama’a da kuma inganta rayuwar ‘yan Najeriya

A cewarsa, an yanke shawarar aiwatar da aikin ne bayan wani umarni da aka bayar bayan ƙaddamar da Babban Aikin Samar da Ruwan Sha na Abuja (Greater Abuja Water Supply Project), wanda ya tanadi cewa dole ne a faɗaɗa hanyoyin samar da ruwa zuwa garuruwan da ke wajen tsakiyar birnin

Tinubu ya bayyana cewa lokacin da Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya gabatar da ƙudirin Aikin Samar da Ruwa na Karu, gwamnatin tarayya ta amince da shi ba tare da ɓata lokaci ba saboda muhimmancinsa ga lafiyar jama’a da bunƙasar tattalin arziki.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *