Ministan Matasa, Ayodele Olawande ya yi martani game da bayanan da ake dangantawa dashi na sauyawa masu bautar kasa kaki.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis 3 ga watan Yuli, Ministan ya ambaci Adire da Ankara ne kawai a matsayin misalin wasu daga cikin shawarwarin da ya gabatar wa gwamnati.

Ayodele yace kawo yanzu, gwamnatin tarayya ba ta yanke hukunci akan wanan batu kamar yadda ake ta yamadidi ba.

Ya bayyana cewa gwamnati na nazarin shawarwari game tsarin da zai dace da kasarnan, ta fuskar ɗorewa, sauƙin amfani, da ƙarancin tsada da kuma fito da martabar ƙasar a idon duniya.

Ministan ya buƙaci ‘yan Najeriya su mayar da hankali kan manyan sauye-sauyen da ake shirin yi wa hukumar kula da masu bautar kasa (NYSC), da suka haɗa da inganta damar samun aikin yi, bunƙasa kasuwanci.

An kirkiri hukumar ta (NYSC)  a shekarar 1976 zamanin gwamnatin mulkin soja, ta Janar Yakubu Gowon.

Sai dai tunda aka kafa ta, babu wasu sauye-sauye masu daukar hankali da aka shirya yi mata kamar irin na wannan lokaci, da ya haifar da cece-kuce daga ciki da wajen kasar.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *