Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Plateau ta bayyana cewa a wani samame na haɗin gwiwa tsakanin ‘yan sanda da sojoji da sauran jami’an tsaro sun daƙile wani yunkurin karya tsaro a harabar cibiyar nazarin manufofi da dabarun ƙasa ta Najeriya (NIPSS) da ke Kuru.
A cewar rundunar, lamarin ya faru ne da misalin karfe 11:23 na dare a ranar 1 ga Yuli, 2026, lokacin da jami’an tsaro ke gudanar da sintiri a harabar cibiyar, sun hangi wani mutum ɗauke da makami yana yawo a kusa da ƙofar shiga ta cibiyar.
Rahotanni sun nuna cewa da mutumin ya ga jami’an tsaron, nan take ya buɗe musu wuta sai dai jami’an tsaron sun mayar da martani cikin kwarewa inda suka yi artabu da shi tare da galaba a kansa lamarin da ya kai ga kashe wanda ake zargin.
Haka kuma an ƙwato bindiga ƙirar AK-47 mai lamba 1969003173 daga hannunsa, yayin da aka kai gawarsa dakin ajiye gawa na asibiti domin gudanar da binciken gawa kamar yadda doka ta tanada.