Shugaba Bola Ahmed Tinubu a ranar Alhamis ya jagoranci wani babban taron tsaro a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.
Taron, wanda aka gudanar a ofishin Shugaban Ƙasa da ke Fadar Gwamnati (State House), yana ɗaya daga cikin tsare-tsare na yau da kullum na sake duba tsarin tsaron ƙasar da kuma ayyukan da ake gudanarwa a halin yanzu domin tunkarar barazanar ta’addanci da fashi da makami.
Jaridar Daily Trust ta gano cewa taron an yi shi ne domin Babban Hafsan Tsaron Ƙasar (Shugaban Ƙasa) ya karɓi sabbin rahotanni kan yanayin tsaro a faɗin ƙasar daga manyan jami’an soja da na hukumomin leƙen asiri.
- Ruwan sama ya lalata gidaje 20 da gonaki a Jihar Plateau
- Faransa 2-0 Moroko: Mbappe ya zura ƙwallo, ya bayar da taimako an ci guda
- Majalisar dattawa ta karanta wasikar da Shugaba Tinubu ya aike mata
Daga cikin waɗanda suka halarci taron akwai: Ministan Tsaro: Janar Christopher Musa (Mai Ritaya) da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaron Ƙasa (NSA): Mallam Nuhu Ribadu da Babban Hafsan Tsaron Ƙasa (CDS): Janar Olufemi Oluyede da Babban Hafsan Sojin Ƙasa (COAS): Laftanal Janar Waidi Shaibu da kuma Babban Hafsan Leken Asiri na Tsaro (CDI): Laftanal Janar Emmanuel Akomaye Undiandeye.
Sauran waɗanda suka halarci taron sun haɗa da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman Kan Tsaron Cikin Gida: Manjo Janar Adeyinka Famadewa da Shugaban Hukumar Leken Asiri ta Ƙasa (NIA): Ambasada Mohammed Mohammed da Shugaban Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS): Adeola Oluwatosin Ajayi.
Kodayake ba a bayyana cikakkun dabarun da aka tattauna a taron da aka yi a bayan fage ba, taron ya ƙara jaddada muhimmancin da gwamnatin Tinubu ke ci gaba da bayarwa ga haɗin gwiwa na kurkusa tsakanin dakarun sarajen ƙasa da hukumomin leƙen asiri wajen magance ƙalubalen tsaron ƙasar.
