Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatinsa ta aiwatar sun fara haifar da sakamako mai kyau, inda ya bayyana cewa tattalin arzikin ƙasar na samun daidaito a hankali.
Tinubu ya bayyana hakan ne yayin taron cin abincin dare da ya yi da wakilan kafafen yaɗa labarai na Fadar Shugaban Ƙasa a Abuja.
Ya ce kuɗaɗen shiga na gwamnati sun ƙaru, jihohi na samun ƙarin kaso daga asusun tarayya, ajiyar kuɗaɗen ƙasar a ƙasashen waje ta inganta, yayin da masu zuba jari ke ƙara nuna amincewa da tattalin arzikin Najeriya.
- ‘Yan Sanda sun daƙile yunƙurin barazanar tsaro a harabar Cibiyar NIPSS
- Babbar Kotun Tarayya ta tabbatar da halaccin shugabancin Sanata David Mark a jam’iyyar ADC
Shugaban ƙasar ya kuma ce an samu ci gaba a fannin tsaro, inda ya bayyana cewa jami’an tsaro sun ƙara ƙaimi wajen yaƙi da ta’addanci, ƴan bindiga, masu garkuwa da mutane da masu satar ɗanyen mai.
Ya ce duk da cewa har yanzu akwai ƙalubalen tsaro, gwamnatinsa ta himmatu wajen tabbatar da zaman lafiya a dukkan sassan ƙasar, tare da gina tattalin arzikin da zai samar wa ‘yan Najeriya ci gaba mai ɗorewa.