Dakarun Operation Hadin Kai tare da haɗin gwiwar kungiyar mafarauta ta Jihar Yobe sun cafke mutane biyar da ake zargi da garkuwa da mutane a ƙaramar hukumar Fune ta Jihar Yobe.
Rundunar ta ce aikin, wanda aka gudanar ranar 23 ga Yuli, 2026 a ƙauyen Jegalari, ya biyo bayan sahihin bayanan sirri kan ayyukan waɗanda ake zargin.
A yayin samamen, sojojin Bataliya ta 233 da ke Damaturu sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 da aka ƙera a gida guda uku da bindiga kirar hannu guda ɗaya da harsasai da kuma wayoyin hannu guda huɗu da ake zargin suna da alaƙa da ayyukan laifi.
- Dole ne Arewa Maso-Gabas ta fi kowa aiki wajen yaƙar ta’addanci— Tinubu
- Na baiwa Muftwang Sa’oi 72 ya janye kalaman sa-Dalung
Waɗanda ake zargin suna hannun sojoji tare da kayayyakin da aka kwato domin ci gaba da bincike kan zargin hannu da suke da shi a ayyukan garkuwa da mutane da sauran laifuka.
Operation Haɗin Kai ta ce za ta ci gaba da gudanar da ayyukan leƙen asiri domin dakile masu aikata laifuka a yankin Arewa maso Gabas, tare da kira ga jama’a su riƙa bayar da bayanan da za su taimaka wajen ƙarfafa tsaro.