Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) da jami’an tsaro su tabbatar da an gudanar da zaɓen gwamnan Osun cikin lumana da gaskiya da adalci.
A cikin wata sanarwa da mai ba shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, ya fitar, Tinubu ya buƙaci masu kaɗa ƙuri’a su fito su gudanar da haƙƙinsu na ɗan ƙasa, tare da guje wa duk wani abu da ka iya kawo cikas ga zaman lafiyar zaɓen.
- Zaɓen Osun: Masu kaɗa ƙuri’a miliyan 1.9 da ƙananan hukumomin da za su iya tantance sakamakon
- Osun 2026: Ɗan takarar mataimakin gwamna na jam’iyyar Accord ya nuna ƙwarin gwiwar samun nasara
Shugaban ya kuma umarci babban sufeton ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro da ke aikin zaɓen da su tabbatar da cikakken tsaro a rumfunan zaɓe, tare da kare jami’an INEC da masu kaɗa ƙuri’a daga barazana ko tsoratarwa.
Tinubu ya ce sakamakon zaɓen gwamnan Osun dole ne ya nuna ra’ayin al’ummar jihar, yana mai buƙatar INEC ta yi amfani da wannan zaɓe na musamman a matsayin gwaji na shirinta gabanin babban zaɓen 2027.
A zaɓen na ranar Asabar, ‘yan takara 15 ne ke fafatawa, ciki har da gwamnan jihar mai ci, Ademola Adeleke, ɗan takarar APC, Asiwaju Munirudeen Bola Oyebamiji, da ɗan takarar ADC, Najeem Salaam.