Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci kafafen yaɗa labarai a Najeriya da su fifita sahihan bayanai maimakon neman jan hankali, yana mai gargadin cewa yaɗa labaran ƙarya da bayanan da ba a tantance ba na iya jefa ƙasa cikin matsala.

Tinubu ya bayyana hakan ne yayin jawabinsa a taron cin abincin dare na farko da ya haɗa shi da wakilan kafafen yaɗa labarai masu bibiyar harkokin Fadar Shugaban Ƙasa da aka gudanar a Abuja.

Ya ce duk da cewa ‘yancin faɗar albarkacin baki da na aikin jarida su ne ginshiƙan dimokuraɗiyya, dole ne a haɗa wannan ‘yanci da ɗaukar nauyin tabbatar da sahihancin bayanai kafin wallafawa.

Shugaban ƙasar ya nuna damuwa kan yadda labaran ƙarya, da bayanan yaudara, da fasahohin ƙirƙirar sauti da hotuna na bogi ke ƙaruwa, yana mai cewa bai kamata ƙwararrun ‘yan jarida su zama hanyar yaɗa bayanan da ba a tantance ba.

Ya ƙara da cewa kafafen yaɗa labarai su zaɓi gaskiya maimakon ƙarya, su fifita ingantattun rahotanni maimakon neman masu kallo ko masu bibiya ta hanyar labaran da ke tayar da hankali.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *