Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya rattaba hannu kan Dokar Zartarwa ta Shugaban Ƙasa kan Daidaita Harkokin Kuɗaɗen Dijital ta shekarar 2026, domin inganta tsarin sa ido da haɗin gwiwa tsakanin hukumomin gwamnati masu kula da wannan fanni.

Sanarwar da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga, ya fitar ta ce dokar ta fara aiki nan take.

Ta ce matakin zai taimaka wajen kare ‘yan ƙasa daga damfara, da hana safarar kuɗaɗe ta haramtacciyar hanya da dakile tallafa wa ta’addanci da kuma kare tsarin kuɗin ƙasar, tare da bai wa sabbin fasahohin dijital damar bunƙasa cikin tsari.

Sanarwar ta ƙara da cewa dokar ba ta kafa sabuwar hukuma ba, illa dai ta samar da tsarin haɗin gwiwa tsakanin hukumomin da suka riga suke da ikon doka a wannan fanni.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *