IMF yace Najeriya ta kashe sama tiriliayan 8 ba tare da bin ƙa'ida ba

Ƴan siyasa sun fara martani game da kalaman IMF cewa gwamnatin Najeriya ta kashe kuɗaɗen da suka kai kusan kashi biyu cikin ɗari na jimillar arziƙin ƙasar.

Wakilin IMF Christian Ebeke ne ya bayyana hakan a Jihar Legas, cewa ƙasar na kashe kuɗaɗe ba tare da bin ƙa’idar dake ƙunshe cikin bayanan kuɗaɗen gwamnati ba.

A cewarsa, yawancin kuɗaɗen sun shafi manyan ayyukan gwamnati da aka gudanar ta hanyoyin da ba su bi tsarin kasafin kuɗi na yau da kullum ba.

Ya ƙara da cewa hakan na kawo cikas wajen tantance yadda aka kashe kuɗaɗen gwamnati, tare da rage bayyana gaskiya a harkokin tafiyar da kuɗaɗen ƙasa.

Sai dai bayanan na IMF sun haifar da martani daga jam’iyyun adawa, inda tsohon mataimakin shugaban Ƙasa Atiku Abubakar, ya buƙaci majalisar dokoki ta Ƙasa da ofishin babban mai binciken kuɗaɗen Gwamnati da kuma hukumomin yaƙi da cin hanci da rashawa su gudanar da cikakken bincike.

Shi kuwa ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar NDC Mista Peter Obi, cewa yake adadin kuɗaɗen da aka ambata ya yi matuƙar yawa, yana mai cewa bai kamata a yi shiru kan batun ba, har sai an gudanar da cikakken bincike tare da sanar da jama’a gaskiyar abin da ya faru.
Masanin tattalin arziƙi, Marcel Okeke, ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da IMF su fayyace tare da daidaita alƙaluman da aka bayyana domin kauce wa ruɗani.
Ya yi gargaɗin cewa idan ba a warware batun cikin gaggawa da kuma bayyana gaskiya ba, hakan na iya ɓata sunan Najeriya.
Okeke yace hakan kuma ka iya jefa shakku a zukatan masu zuba jari a cikin gida da ƙasashen waje, domin rage amincewar su ga nagartar da ake iƙirarin tattalin arziƙin ƙasar na da shi.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *