Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta mayar wa ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar AAC, Omoyele Sowore, belinsa tare da ba shi sabon beli na Naira miliyan 200.

Mai shari’a Muhammad Umar ya yanke hukuncin ne a ranar Talata, inda ya ce Sowore zai gabatar da mutane biyu da za su tsaya masa kafin a bashi belin.

Kotun ta ce ɗaya daga cikin masu tsaya masa dole ne ya kasance sarki ko shugaban gargajiya daga garinsu, yayin da na biyun kuma dole ne ya mallaki kadara a Babban Birnin Tarayya Abuja.

Kotun ta kuma umarci Sowore da ya miƙa fasfot ɗinsa ga magatakardar kotu har zuwa lokacin da za a kammala shari’ar.

Ana tuhumarsa ne kan laifuffuka biyar da suka shafi zargin aikata laifukan yanar gizo, bayan wani furuci da ya yi kan Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.

A ranar 16 ga watan Yuni ne kotun ta soke belinsa tare da bayar da sammacin kama shi, bayan da ya gaza halartar zaman kotu.

Daga bisani ya miƙa kansa ga kotun a ranar 22 ga watan Yuni, inda ya nemi a janye Mai shari’ar daga shari’ar, amma kotun ta yi watsi da buƙatar tare da tsare shi a Gidan Gyaran Hali na Kuje.

Sai dai a zaman kotun na ranar Talata, Mai shari’a Muhammad Umar ya amince da sabuwar buƙatar belin Sowore, tare da mayar masa da belinsa bisa sharuɗɗan da kotun ta gindaya.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *