Ƙungiyar Amnesty International ta Najeriya ta yi Allah wadai da abin da ta bayyana a matsayin ƙaruwar ɗaukar doka a hannu a wasu sassan Arewacin Najeriya, tana mai cewa hakan na barazana ga bin doka da oda.

A cikin wata sanarwa, ƙungiyar ta yi nuni da lamarin da ya faru a ranar Laraba 1 ga Yulin 2026 a unguwar Kofar Soro da ke birnin Katsina, inda ta ce taron yara da matasa dauke da makamai suka kewaye kotu suna neman a kashe wani mutum da ake yi wa shari’a kan zargin yin saɓo ga addini, ba tare da bin tsarin shari’a ba.

Amnesty ta kuma ambaci kisan Ummulkhairi, wata malama kuma uwa mai ‘ya’ya biyar da aka ƙone a Mararabar Jos da ke jihar Kaduna, sakamakon zargin da ƙungiyar ta ce ba a tabbatar ba na yunƙurin sace yara, lamarin da ya faru kimanin kwanaki goma kafin abin da ya faru a Katsina.

Ƙungiyar ta bayyana cewa irin waɗannan hare-hare na nuna ƙara samun rashin bin doka da kuma raina tsarin shari’a, tana mai jaddada cewa duk wanda ake zargi da aikata wani laifi yana da haƙƙin samun adalci ta hanyar shari’a kamar yadda kundin tsarin mulkin Najeriya ya tanada.

Amnesty International ta buƙaci gwamnatin jihar Katsina da hukumomin tsaro su gudanar da cikakken bincike kan lamarin, tare da gurfanar da duk wanda ake zargi da tayar da tarzoma ko ɗaukar doka a hannu, tana mai cewa adalci na gaskiya yana samuwa ne ta hanyar bin doka, ba ta hanyar tashin hankali ko hukuncin taron jama’a ba.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *