Babban Daraktan Hukumar Asusun Bunƙasa Kayayyakin Iskar Gas ta Tsakiya da Ƙasa (MDGIF), Oluwole Adama, ya jaddada muhimmancin bunƙasa kasuwar iskar gas ta cikin gida domin haɓaka tattalin arziki da ci gaban masana’antu a Najeriya.

Adama ya bayyana haka ne yayin wani zaman tattaunawa mai taken “Bunƙasa Kasuwar Iskar Gas ta Cikin Gida domin Haɓaka Tattalin Arziki da Ci Gaba”, a rana ta uku ta taron Makon Makamashin Mai da Gas na Najeriya (NOG Energy Week 2026), da aka gudanar a Cibiyar Taro ta Ƙasa da Ƙasa (ICC) da ke Abuja.

Ya ce ƙara zuba jari a kayayyakin more rayuwa na iskar gas, da inganta damar shiga kasuwa da kuma haɗin gwiwa tsakanin gwamnati, da masu zuba jari da kamfanoni masu zaman kansu zai taimaka wajen cin gajiyar ɗimbin albarkatun iskar gas da Najeriya ke da su.

Adama ya ƙara da cewa bunƙasa kasuwar iskar gas zai ƙarfafa samar da makamashi, da haɓaka masana’antu da samar da ayyukan yi da kuma inganta gasa a tattalin arziƙin ƙasar.

Ya kuma tabbatar da cewa hukamar MDGIF za ta ci gaba da tallafa wa zuba jari a fannin iskar gas ta hanyar sabbin hanyoyin samar da kuɗi da haɗin gwiwa, domin cimma manufofin Gwamnatin Tarayya na Shekarun Iskar Gas (Decade of Gas Initiative) da kuma sauyin amfani da makamashi.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *