Ƙungiyar Kasuwanci ta Nahiyar Afirka, AfCFTA, ta amince da tsarin zamani da Najeriya ta samar domin inganta ayyukan Kwastam, inda wani kamfanin Najeriya ya samu aikin zamanantar da harkokin Kwastam a wasu ƙasashen Afirka na tsawon shekaru 20.

Kamfanin Bergmans, ta hannun reshensa na AfriTrade CMP Limited, zai aiwatar da aikin da ya haɗa da amfani da fasahar zamani wajen bibiyar kaya da kula da iyakokin ƙasashe da inganta ayyukan Kwastam da musayar bayanan cinikayya.

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce amincewar AfCFTA da tsarin Najeriya na nuna cewa ƙasar na da damar samar da hanyoyin fasaha da za su amfani sauran ƙasashen Afirka.

Babban Sakataren AfCFTA, Wamkele Mene, ya kuma bayyana tsarin B’Odogwu, wanda Hukumar Kwastam ta Najeriya ke amfani da shi, a matsayin abin koyi ga sauran ƙasashen Afirka.

Ya ce zaɓar tsarin da kamfanonin Afirka suka samar na ƙara tabbatar da muhimmancin ƙwarewa da kirkire-kirkire daga cikin nahiyar.

Shugaba Tinubu ya ce Najeriya a shirye take ta ba da gudunmawarta wajen ganin kayayyaki na iya ratsa iyakokin ƙasashen Afirka cikin sauri, da ƙarancin kuɗi da kuma rage matsalolin cinikayya.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *