Sheikh Ahmad Gumi ya bayyana cewa ya kamata a yi wa Sheikh Sani Yahaya Jingir uzuri kan matsayinsa mai tsauri a harkokin siyasa, yana mai cewa malamin na fuskantar matsanancin nuna wariya ga Musulunci a jihar da yake.

Gumi ya bayyana hakan ne a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya ce Sheikh Jingir yana cikin tsakiyar guguwar tsananin nuna ƙiyayya da wariya ga Musulunci.

Hakan dai ya biyo bayan wani batu da sheik Jingir yayi a yayin da yake jawabi a wurin bikin auran gata da gwamntin jihar kano ta shirya.

A yayin taron, Sheikh Jingir ya ce ɗan takarar da yake goyon baya shi ne Bola Ahmed Tinubu, saboda ya zabi Musulmi a matsayin mataimakinsa.

A cewarsa, yana daga cikin waɗanda suka yi kira ga jama’a da su goyi bayan tikitin Musulmi da Musulmi a zaben 2023, yana mai tambayar, ko laifi ne ya goyi bayan irin wannan tikiti a matsayinsa na Musulmi mai wa’azin addinin Islama.

Sai dai kalaman nasa sun jawo suka daga wasu ’yan Najeriya, waɗanda suka bayyana su a matsayin yin amfani da matsayinsa na malamin addini wajen tallata wani ɗan takarar siyasa, abin da suka ce zai iya cutar da martabar Musulunci a ƙasar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *