Ƙungiyar Musulmi ta Duniya, tare da haɗin gwiwar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), za ta gudanar da taron tsaron ƙasa da ƙasa a Abuja, domin tattauna hanyoyin ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kan ƙasa da tsaro.

Taron da za a gudanar a ranar Talata, 11 ga Agusta, a Cibiyar Taro ta Ƙasa da Ƙasa ta Bola Ahmed Tinubu da ke Abuja, zai haɗa malaman addini da masu tsara manufofi da sauran masu ruwa da tsaki.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya ce taron zai mayar da hankali kan alaƙar da ke tsakanin zaman lafiya da tsaro da bunƙasar tattalin arziki, tare da ƙarfafa fahimtar juna tsakanin Musulmi da Kiristoci da sauran mabiya addinai.

Ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya jajirce wajen tabbatar da zaman lafiya da jituwa tsakanin addinai da haɗin kan ’yan Najeriya, yana mai cewa zaman lafiya da tsaro su ne ginshiƙan ci gaban ƙasa.

Shi ma Babban Sakataren kungiyar Muslimi ta Duniya, Sheikh Mohammed bin Abdulkarim Al-Issa, ya yaba da ƙoƙarin Shugaba Tinubu na inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin Musulmi da waɗanda ba Musulmi ba.

Sheikh Al-Issa ya ce zaman lafiya a Najeriya zai taimaka matuƙa wajen ƙarfafa tsaro da kwanciyar hankali a Yammacin Afirka da ma duniya baki ɗaya.

Ministan ya kuma bayyana ziyarar Sheikh Al-Issa a matsayin wata alama ta ƙarfafa alaƙar Najeriya da Saudiyya da sauran ƙasashen duniya.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *