Daga dama: Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso, Cif Seriake Dickson, Mista Peter Obi yayain ganawarsu kan komawar shugabannin adawar NDC (Hoto: Punch)

Daruruwan magoya bayan tafiyar Kwankwasiyya da ta Obidients ne suka yi rajista da jam;iyyar National Democratic Congress (NDC) da maraicen ranar Lahadi, kwana biyu kafin cikar wa’adin rajista da jam’iyyu ga masu son tsayawa takara.

Jagoran Kwankwasiyya, tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ya tabbatar da haka a lokacin da jigogin adawar na Najeriya suka yanki katin NDC din, ya kuma ce sun yanke shawarar dunguma su shiga jam’iyyar ne ganin cewa wa’adi na daf da cika.

“Ganin cewa kwana biyu kacal suka rage don yin rajista, shi ya sa muka yanek shawarar cewa wajibi ne mu yanki katin gaba dayanmu a yau da yardar Allah”, inji Kwankwaso.

Jam’iyyar ta NDC dai tana karkashin jagorancin tsohon Gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Serikae Dickson, ne.

Tun da farko dai an ba da rahoton cewa ranar Litinin ko Talata ne jagororin adawar biyu za su sanar da makomarsu a siyasance.

Sauyin shekar ’yan takarar shugabancin kasar a 2023 daga ADC dai ya tabbatar da takarar Obi da Kwankwaso a karkashin inuwa daya a 2027, ya kuma jefa gamayyar ’yan adawa don kalubalantar APC a cikin rudani.

Ranar 7 ga watan Maris ne dai Mista Peter Obi ya shiga jam’iyyar ADC yayin da Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso ya shiga ranar 30 ga watan na Maris.

Jagororin adawar sun bayyana rikice-rikicen cikin gida da shari’o’in da suka dabaibaye ADC a matsayin dalilinsu na ficewa daga jam’iyyar.

Akwai kuma zarge-zargen da magoya bayansu suka yi cewa an gina ADC ta yadda za ta ba da fifiko ga wani dan Takara guda.

A nasa jawabin bayan shigar su NDC, Peter Obi ya kuma zargi Gwamnati da kunna wutar rikice-rikice a jam’iyyun adawa.

“Gwamnati mai ci a yanzu ta tabbatar da kunno wutar rikice-rikice marasa iyaka a jam’iyyunmu, lamarin da ya tilasta mana barin jam’iyyun mu koma wata jam’iyya da tunanin abin zai yi sauki.

“Amma sai muka ga ashe mun yi gudub gara ne mun fada wa zago, [shi ya sa] a yau muka bar can muka dawo NDC, inda jagoranta ya shaida mana babu kararraki a kotu”, inji Obi.

Ya kuma yi kira ga ’yan jam’iyya da kada su je kotu, a maimakon haka su zage dantse don gina jam’iyyar tasu.

Yayin da wannan sauyin shekar ya karfafa NDC da samun karuwar hamshakan jagororin adawa biyu da ’yan majalisar dokoki da dama, ya kuma raunata karfin ADC wadda da ma tuni takaddamar shugabanci da shari’o’I suke namn durkusar da ita.

Ko da yake ana ganin Obo da Kwankwaso suna da goyon bayan matasa da mata, wasu manzarta suna ganin kayar da APC a zaben 2027 yana bukatar hadewar daukacin ’yan adawa a karkashin inuwa daya.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *