Jami’an Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arzikin Ƙasa Ta’annati ta Najeriya (EFCC) shiyyar Abuja, sun kama wasu mutane 17 da ake zargi da aikata damfarar yanar gizo a ranar Talata, 17 ga Yuli, 2025.
An kama waɗanda ake zargin ne a yankin Mararaba da ke Jihar Nasarawa, bayan samun sahihan bayanan sirri da ke nuna cewa suna da hannu a ayyukan damfarar da suka shafi amfani da yanar gizo.
- Bidiyon ‘yanbindiga na gaisawa da ɗansanda ba gaskiya bane – ‘Yansanda
- Majalisar Tarayya ta sake tsawaita aiwatar da kasafin 2025 zuwa Satumba
- Ƙudirin kafa ƴan sandan jihohi ya samu sabon ci gaba, bayan da Majalisar Dattawa ta amince da shi.
Kayan da aka ƙwato daga hannunsu sun haɗa da motoci biyar, wayoyin hannu 20 da kuma kwamfyutocin tafi-da-gidanka guda huɗu.
Hukumar tace da zarar ta kammala bincike za ta gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu.