Shugaban ya bukaci majalisar ta gaggauta gyaran daftarin dokar ba tare da bata lokaci ba

Gwamnatin Tarayya ta kafa Majalisar Kula da Harkokin Kuɗaɗen Dijital domin haɗa kai tsakanin hukumomin da ke sa ido kan kasuwar kadarorin dijital a Najeriya.

A ƙarƙashin sabon tsarin, Babban Bankin Najeriya (CBN) ne zai jagoranci majalisar, yayin da Hukumar Tara Kuɗaɗen Shiga ta Ƙasa (NRS) da Hukumar Kula da Kasuwar Hannayen Jari (SEC) za su kasance mataimakan shugabanni.

Sauran mambobin majalisar sun haɗa da Hukumar Binciken Kuɗaɗen Sirri (NFIU) da kuma Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro (ONSA).

Majalisar za ta tsara manufofi, ta ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomin, tare da aiki da Babban Lauyan Tarayya wajen samar da tsarin doka guda da zai dace da manufofin tsaro da tattalin arzikin Najeriya.

A sanarwar da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar ta ce tsarin zai fara aiki nan take.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *