Al’ummar Zambiya za su fito ranar 13 ga Agusta domin kada kuri’a a babban zaben kasar, wanda ake kallon sa a matsayin gwajin ko sauye-sauyen tattalin arziki da aka kwashe shekaru ana aiwatarwa sun haifar da sauki a rayuwar yau da kullum.

A cewar Hukumar Zabe ta Zambiya, kimanin masu kada kuri’a miliyan 8.79 ne suka yi rajista domin zaben.

‘Yan takara 14 ne ke neman kujerar shugaban kasa, ciki har da Hakainde Hichilema, shugaban jam’iyyar United Party for National Development (UPND) mai mulki, wanda ke neman wa’adi na biyu.

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa ta tura jami’an tsaro kimanin 25,000 jihar Osun –
An yanke wa Bashar al-Assad hukuncin kisa

Haka kuma akwai Brian Mundubile, dan takarar shugaban kasa na kawancen jam’iyyun adawa na Tonse Alliance.

Gwamnatin Hichilema ta ce an samu ci gaba wajen sauye-sauyen tattalin arziki, ciki har da sake tsara bashin kasar da kuma kammala shirin tallafin Asusun Lamuni na Duniya (IMF).

Bayanan Hukumar Kididdiga ta Zambiya sun nuna cewa hauhawar farashin kayayyaki ta ragu zuwa kashi 6.8 cikin 100 a watan Afrilu.

Sai dai tsadar abinci, man fetur da wutar lantarki na ci gaba da jefa matsin lamba kan iyalan kasar.

Joan Chirwa, mai fafutukar kare hakkin bil’adama kuma gogaggiyar ‘yar jarida a Zambiya, wadda ta kafa kungiyar Free Press Initiative, ta ce har yanzu da dama daga cikin ‘yan kasar ba su ga sauyi mai ma’ana a rayuwarsu ta yau da kullum ba.

Ta ce babban abin da masu kada kuri’a ke tambaya shi ne ko sauye-sauyen tattalin arzikin da Hichilema ya aiwatar a wa’adinsa na farko sun haifar da karuwar kudaden shiga da kuma inganta yanayin rayuwar iyalai.

“Tambayar da ta fi tasowa daga masu kada kuri’a ita ce ko sauye-sauyen tattalin arziki na wa’adin farko na Hichilema sun sauya zuwa ingantuwar kudaden shiga da yanayin rayuwar iyalai,” in ji Chirwa.

Ta amince cewa an samu ci gaba wajen sake tsara bashin Zambiya da kuma shirin IMF.

Sai dai ta ce samun daidaito a manyan alamomin tattalin arziki ba lallai ne ya haifar da ingantuwar jin dadin iyalai kai tsaye ba, musamman ganin yadda tsadar abinci, man fetur da wutar lantarki ke ci gaba da yi wa jama’a nauyi.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *