NCDC ta tada hankali kan barazanar ebola a Najeriya

NCDC ta ƙara matakan rigakafin Ebola yayin da haɗarin shigowarta Najeriya ke ƙaruwa.

Hukumar Cututtuka ta Najeriya ta ce haɗarin shigowar Ebola ya ƙaru ne saboda yaduwa a Gabashin Afirka da zirga-zirgar mutane.

Darakta-Janar na Hukumar, Dakta Jide Idris, ya ce duk da babu Ebola a Najeriya, ana ƙara matakan kariya da sa ido a iyakoki da dakunan gwaje-gwaje.


Ya kuma ja hankalin Jihohi da ma’aikatan lafiya su ƙara shiri da horo don gano cutar cikin gaggawa tare da haɗin gwiwa don kare Najeriya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *