Dakarun Operation Hadin Kai sun dakile wani hari da mayakan ISWAP suka kai sansanin sojoji na Mandaragírau, a ƙaramar hukumar Biu ta jihar Borno.

Harin ya faru da misalin ƙarfe 2:00 na dare ranar 15 ga Agusta 2026, inda mayakan suka kai farmaki daga ɓangarori biyu. Sai dai sojojin Bataliya ta 162 sun gano harin ta hanyar na’urorin sa ido, tare da tura dakarun da suka dakile masu harin.

Rundunar ta ce an kashe da dama daga cikin mayakan, yayin da aka kwato bindigogin AK-47 da harsasai da na’urar harba rokoki RPG da bama-bamai da wasu kayan yaƙi.

Hotunan na’urorin sa ido sun kuma nuna wasu mayakan suna jan gawarwakin abokan aikinsu zuwa yankin Timbuktu Triangle.

Rundunar ta ce babu wani soja da ya rasa ransa ko jikkata a yayin harin.

Operation Hadin Kai ta ce za ta ci gaba da kai hare-hare da dakile ayyukan ‘yan ta’adda domin hana su samun damar gudanar da hare-hare tare da dawo da zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *