Hedkwatar Rundunar Haɗin Gwiwa ta Arewa Maso Gabas, wadda ake yiwa lakabi da Operation Hadin Kai (OPHK), a ƙarƙashin Operation Desert Sanity V, ta ceto fararen hular da aka yi garkuwa da su a yankin Amuda dake Ngoshe a Jihar Borno
A wata sanarwa da ya fitar, Kakakin Rundunar Laftanar Kanar Sani Uba, ya ce dakarun OPHK sun yi nasarar kubutar da mutane biyu da aka yi garkuwa da su daga al’ummar Ngoshe.
Waɗanda aka ceto sun haɗa da Maryam Muhammad mai shekaru 20 da ɗanta Bello Muhammad mai shekara 1 da wata 4
Binciken farko ya nuna cewa an tsare su ne a wani sansanin ’yan ta’adda da ke cikin tsaunukan Mandara, amma suka samu damar tserewa bayan munanan hare-haren soji kan maboyar ’yan ta’addan, wanda ya tilasta masu garkuwar guduwa su bar mutanen
Sanarwar ta kara da cewa waɗannan nasarori na nuna irin tasirin hare-haren da dakarun Operation HADIN KAI ke ci gaba da kaiwa, da kuma yadda tsarin tallafawa ’yan ta’adda ke kara raunana, musamman a yankunan tsaunukan Mandara da al’ummomin kan iyaka.
Rundunar Haɗin Gwiwar ta sake tabbatar wa jama’a da kudurinta na ci gaba da matsa wa ’yan ta’adda lamba, ceton waɗanda aka yi garkuwa da su, da kuma dawo da zaman lafiya, tsaro da bunƙasar tattalin arziki mai ɗorewa a yankin Arewa maso Gabas.
Babban Hafsan Sojin Najeriya ya yaba wa dakarun bisa irin bajintar da suka nuna a fagen daga, tare da ƙarfafa musu gwiwa da su ci gaba da wannan ƙwazo domin kare ƙasa.
