Mai Girma Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a na Ƙasa, Mohammed Idris, ya sake jaddada aniyar Gwamnatin Tarayya na ƙarfafa tsaro da yanayin yaɗa labarai da suka dace domin gudanar da zaɓuka masu zaman lafiya, gaskiya da amintakka a shekarar 2027.
Ministan ya bayyana haka ne ranar Talata a birnin Abuja, yayin Babban Jawabi na 8, Shirin Tasiri, da kuma Lambobin Yabo na Karramawa da Kamfanin Jaridun Blueprint ya shirya, mai taken: “Ƙalubalen Tsaro da Amincin Zaɓukan Najeriya na 2027.”
Idris ya yaba wa jaridar Blueprint saboda dorewar wannan babban taro na shekara-shekara, inda ya bayyana shi a matsayin muhimman dandalin da ke ba masu tsara manufofi, ƙwararru, masana, kafafen yaɗa labarai, da sauran masu ruwa da tsaki damar tattauna batutuwan da suka shafi ci gaban ƙasa.
Ya bayyana cewa taken taron ya zo a daidai lokacin da ya dace, yana mai cewa amincin zaɓe ba wai kawai ranar jifan ƙuri’a ake gina shi ba, har ma da yanayin tsaro, mutuncin hukumomi, halayyar ‘yan siyasa, ƙwarewar kafafen yaɗa labarai, da kuma ingancin bayanan da ke gaban ‘yan ƙasa.
“Ga gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, tsaro da walwalar ‘yan Najeriya su ne manyan ayyukan da gwamnati ta sa a gaba,” in ji Ministan. Ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da tattara kayan aiki, jami’ai, da fasahohin da ake ƙata domin fuskantar ta’addanci, fashi da makami, garkuwa da mutane, da sauran barazana ga amincin ‘yan Najeriya.
Haka kuma, Ministan ya fito da batun barazanar da ke ƙara girma ta hanyar yaɗa labaran ƙarya da ɓatanci, musamman ma tare da saurin haɓakar Fasahar Haƙƙon Ɗan-adam (Artificial Intelligence), wanda ya sauƙaƙa ƙirƙirar sautuka, bidiyoyi, da hotuna na ƙarya amma masu gamsarwa.
“Dimokuraɗiyya ba za ta iya dorewa ba a inda ake gangan ana ɓatar da ‘yan ƙasa,” in ji Idris. Ya bayyana cewa Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a ta Ƙasa, cikin haɗin gwiwa da hukumar UNESCO da sauran masu ruwa da tsaki, ta kafa Cibiyar Koyon Yaɗa Labarai da Wayar da Kai ta Ƙasa (IMILI) a Abuja don ƙarfafa fahimtar kafafen yaɗa labarai da bayanai.
Babban Manajan Darakta/Shugaban Gudanarwa na Kamfanin Jaridun Blueprint, Salisu Umar, ya ce an kafa wannan babban jawabi na shekara-shekara, wanda aka fara tun a shekarar 2018, ne domin samar da dandali na tattauna batutuwan da suka shafi bukatun ƙasa bayan shafukan jaridu na yau da kullum, tare da karrama ‘yan Najeriya da suka nuna shugabanci na gari da tasiri mai kyau.
Shugaban Taron, tsohon Gwamnan Jihar Zamfara kuma Sanata mai wakiltar Shari’ar Sanatan Yammacin Zamfara, Sanata Abdul’Aziz Yari Abubakar, ya ce kada a bar maganar rashin tsaro a matsayin aikin hukumomin tsaro kaɗai. Ya jaddada cewa dole ne shugabannin siyasa, al’ummomi, ‘yan ƙasa, da sauran masu ruwa da tsaki su taka tasu rawar.
Yayin da yake tsakuro tarihi daga gogewarsa a gwamnati, Sanata Yari ya ce ƙalubalen rashin tsaro ya dore a gwamnatoci da lokutan zaɓe daban-daban, kuma ya yi gargaɗi game da mayar da lamarin na siyasa.
“Maganar rashin tsaro ba abin da za a yi ciniki da shi ba ne don kawai a sace zukatan ‘yan ƙasa,” in ji shi, yana mai kiran ‘yan Najeriya da su haɗu baki ɗaya su fuskanci ƙalubalen kuma su yi aiki don ganin ƙasar ta kasance mafi aminci ga tsara na yanzu da na gobe.
Uban Ƙasa na Ranar, Mai Martaba Alhai (Dr.) Yahaya Abubakar, CFR, Etsu Nupe, wanda Mai Martaba Alhaji Ahmadu Aliyu Oga Onawo, Andoma na Doma ya wakilta, ya yaba wa jaridar Blueprint saboda gudunmawar da take bayarwa ga muhawarar ƙasa, kuma ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su ci gaba da jajircewa ga haɗin kai da ci gaban ƙasar.
A cikin saƙonsa, Etsu Nupe ya jaddada cewa kada ƙalubalen Najeriya su rage gagarumin tasiri na ɗan-adam da na ilimi da ƙasar ke da shi, inda ya bayyana cewa “babu wani madadin Najeriya mai haɗin kai” kuma ya bukaci ‘yan Najeriya da su ɗauki alhakin gina ƙasa mafi ƙarfi da wadata.
Babban Mai Jawabi, Mai Girma Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (Mai Ritaya), wanda Manjo Janar O.T. Akinjobi ya wakilta, ya ce sauyawar yanayin tsaro na buƙatar kyakkyawar dabarar tsaron zaɓe gabanin Babban Zaɓen 2027.
Ya bayyana cewa tsaron zaɓe ba zai ƙara tsayawa ga kare rumfunan zaɓe da kayayyakin zaɓe kaɗai ba, domin barazanar da ke ɓoyewa yanzu sun haɗa da katsalandan ta yanar gizo (cyber interference), yaɗa labaran ƙarya, ɓatanci, da ƙoƙarin rage amon jama’a ga hukumomin dimokuraɗiyya.
“Ba za a ƙara kallon tsaron zaɓe kawai a matsayin kare rumfunan zaɓe ba. Shashen kare halaccin dimokuraɗiyya ne gaba ɗaya,” in ji shi, yana mai kiran da a gudanar da tsarin tsaro na sirri (intelligence-led), ingantaccen tsaron yanar gizo, haɗin gwiwar hukumomi, sadarwa ta dabara, da kuma ƙarin shigar ‘yan ƙasa da baki ɗaya.
Ministan Yaɗa Labarai ya taya jaridar Blueprint, masu jawabi, da waɗanda suka karɓi Lambobin Yabo na Karramawa murna, yana mai jaddada cewa amincewa da gagarumar gudunmawa ga ci gaban ƙasa zai ƙarfafa ci gaba da jajircewa ga aikin gwamnati da ƙwarewa.
Ya nuna kyakkyawan zato cewa hukumomin dimokuraɗiyya na Najeriya za su ci gaba da ƙarfafa, yayin da ya sake jaddada aniyar Gwamnatin Tarayya ga zaman lafiya, kwanciyar hankali, haɗin kan ƙasa, da ci gaba mai dorewa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *