Rahotanni sun ce jami’an tsaro sun kama sama da mutane 100 da ake zargin an shigo da su domin su kada kuri’a a zaɓen gwamnan jihar Osun da ake gudanarwa yau, Asabar.
An ce mutanen, waɗanda ke ɗauke da sabbin katunan zaɓe na dindindin (PVC), an boye su a gidan wani ɗan jam’iyyar Accord Party mai suna Hon. Abiola Ibrahim, gabanin fara zaɓen.
- Zaɓen Osun: An tura DIG, Kwamishinonin Yanansanda 30, da jami’ai 15,000
- Yaduwar ƙwayoyin cuta masu jure maganin rigakafi na ƙara zama barazana ga Duniya
Wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta ya nuna yadda jami’an tsaro ke yi wa waɗanda aka kama tambayoyi kan dalilin kasancewarsu a wurin da kuma manufar zuwansu jihar.
A yayin tambayoyin, an rawaito cewa Abiola Ibrahim ya amince cewa an mutanen ne a gidansa domin su kada kuri’a ga jam’iyyar Accord Party a zaɓen.
Rahotanni sun ce Ibrahim ɗan Majalisar Dokokin Jihar Osun ne mai wakiltar mazabar Irewole-Isokan.
Sai dai har zuwa lokacin fitar rahoton, ba a samu wata sanarwa daga Rundunar ’Yan Sandan Jihar Osun da ta tabbatar ko ta yi karin bayani kan kama mutanen ba.